Posts

Showing posts from July, 2023

Taskar Ahlul Baitin-Nabiy (s).

Image
     ☆via-the2brothers-links☆ Da Sunan Allah Mai Rahama Mai jin kai. Imam Ali (A.S) Yana cewa:  "Ka tsare harshenka kamar yadda kake tsare dukiyarka. Domin sau da yawa wata maganar tana kore alheri. Wata maganar kuma tana janyo sharri". Imam Ali (A.S) Yana cewa: "Babbar hanyar zama lafiya itace sallamawa ga iko da kaddarar ubangiji". Imam Ali (A.S) Yana cewa: "Jure masifa jarumta ce kamun kai arzikine. Tsare kai daga sabon Allah shine babbar garkuwa".   Imam Ali (A.S) Yana cewa: "Talauci yana nakasa hujjar ma'abocin hankali. Talaka yakan zama bako a garin haihuwarsa." Imam Ali (A.S) Yana cewa: "Kada kaji kunya ko nauyin bayar da kadan. Domin hana kadan din yafi bayar da kadan din karanta.   Imam Ali (A.S) Yana cewa: "Mai aikata kyakkyawan aiki yafi kyakkyawan aikin kyau kamar yadda mai aikata mummunan aiki yafi mummunan aikin muni". Imam Ali (A.S) Yana cewa: "Lafiyar jikinka tana karuwa idan hassadarka tana raguwa". I

Taskar Ahlul Baitin-Nabiy (s).

Image
     ☆via-the2brothers-links☆   Da Sunan Allah Mai Rahama Mai jin kai. -HADISAI GOMA DAGA IMAM BAQIR (AS): 1- Imam Baqir (AS) Yace:  "Farkon Abin da Za'a Yiwa Bawa Hisabi Dashi Itace Sallah, Idan ta Ƙarɓu to Dukkan Sauran Ayyukan Bawa Za'a Karbe su. - Bihar 7/267. 2- Imam Baqir (AS) Yace:  "Hadisan mu (Maganganunmu) Suna Raya Zukata Ne". - Bihar 2/144. 3- Imam Baqir (AS) Yace:  "Duk Wanda Ya Kasance Mai Biyayya ga Allah (T) to shi Masoyinmu Ne. Hakanan Kuma Wanda Ya Kasance Mai Saɓawa Allah to Shi Maƙiyinmu Ne." - Alkafiy 2/75. 4- Imam Baqir (AS) Yace:  "Ku Nemi ilimi, Domin Nemansa Abu ne Mai Kyau Kuma Koyonsa Ibada Ce." - Biharul Anwar 74/189. 5- Imam Baqir (AS) Yace:  "Me Tuba Daga Zunubai Kamar Wanda Bashi da Zunubai Ne Kwata-Kwata" - Wasa'il 16/74. 6- Imam Baqir (AS) Yace:  "Ya Wajaba ga Mumini Akan Ɗan Uwansa Mumini Ya Ɓoye (Sirranta) Masa Manya Manyan Zunubansa Guda Saba'in (70) Daga Sanin Mutane." - Bihar 7

Taskar Ahlul baitin-Nabiy (s)

Image
Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai. 📜 دعاء الفرج ”إلـهي عَظُمَ الْبَلاءَ، وَبَرِحَ الْخَفاءُ، وَانْكَشَفَ الْغِطاءُ، وَانْقَطَعَ الرَّجاءُ، وَضاقَتِ الأرض، وَمُنِعَتِ السَّماءُ، واَنْتَ الْمُسْتَعانُ، وَاِلَيْكَ الْمُشْتَكى، وَعَلَيْكَ الْمُعَوَّلُ فِي الشِّدَّةِ والرَّخاءِ، اَللّـهُمَّ صَلِّ عَلى مُحَمَّد وَآلِ مُحَمَّد، اُولِي الأمر الَّذينَ فَرَضْتَ عَلَيْنا طاعَتَهُمْ، وَعَرَّفْتَنا بِذلِكَ مَنْزِلَتَهُمْ، فَفَرِّجْ عَنا بِحَقِّهِمْ فَرَجاً عاجِلًا قَريبًا كَلَمْحِ الْبَصَرِ اَوْ هُوَ اَقْرَبُ، يا مُحَمَّدُ يا عَلِيُّ يا عَلِيُّ يا مُحَمَّدُ اِكْفِياني فَاِنَّكُما كافِيانِ، وَانْصُراني فَاِنَّكُما ناصِرانِ، يا مَوْلانا يا صاحِبَ الزَّمانِ، الْغَوْثَ الْغَوْثَ الْغَوْثَ، اَدْرِكْني اَدْرِكْني اَدْرِكْني، السّاعَةَ السّاعَةَ السّاعَةَ، الْعَجَلَ الْعَجَلَ الْعَجَل، يا اَرْحَمَ الرّاحِمينَ، بِحَقِّ مُحَمَّد وَآلِهِ الطّاهِرينَ.“ • مفاتيح الجنان   Wasu Daga Cikin Zantuka/Hadisai Na Imam Mahdi (Ajjalallahu Ta'ala Farjahu): 1. Al-Imamul Mahdi (a.f)  yana cewa:  "Hakika a Alj